Gwamnan jihar California ya caccaki Amurka kan munanan hare-haren da kasar ke kai wa kan jiragen ruwa da take zargin ana fataucin miyagun ƙwayoyi a yankin Caribbean.
Da yake magana a taron Sauyin yanayi na COP30 a Brazil, Mr Newsom ya ce abin takaici ne ganin yadda Amurka take kai hari kan jiragen ruwa ba tare amincewar majalisa ba.
Amurka yanzu ta kai hari kan jiragen ruwa 19, tare da kashe mutum 80. A ranar Talata ne wani babban jirgin ruwan yakin Amurka ya isa yankin.
Shugaban Colombia Gustavo Petro ya ce ya bayar da umarnin dakatar da musayar bayanan sirri tsakanin kasarsa da Amurka, yayin da Amurka ke ci gaba da luguden wuta









