Home Afrika Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 18 daga hannun ‘yanbindiga a gaɓar tekun...

Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 18 daga hannun ‘yanbindiga a gaɓar tekun Kamaru

80
0

Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 18 daga hannun ‘yanbindiga a gaɓar tekun Kamaru

Manjo Sokoya ya ce nan-take dakarun Birged ta 13 da ke aiki a Ikang suka bi sawun ‘yanfashin tekun, inda suka yi ta musayar wuta lamarin da ya sa ɗaya daga cikin kwalekwalensu ya kife.

Sarkin Musulmi Ya Yaba wa Sojoji kan tsoro

’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 a Jihar Filato

Sojojin Najeriya Sun Daƙile Harin Ƴanbindiga a Bitta, Borno, Sun Hallaka Wasu da Makamai da Kayayyaki da Aka Kwato

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarunta na Birged ta 13 sun yi nasarar ceto mutum 18, ciki har da ƙananan yara biyu, bayan ‘yanbindiga sun yi garkuwa da su a kwalekwale yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Kamaru.

Wata sanarwa da mataimakin mai magana da yawun Birged ta 13 Manjo Yemi Sokoya ya fitar ranar Litinin ta ce lamarin ya faru ne ranar Lahadin da ta wuce.

Ya ƙara da cewa wasu da ake zargi ‘yanfashin teku ne a cikin kwalekwale guda biyu masu gudun tsiya da kwalekwale na katako sun yi garkuwa da wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji 18 da ke kan hanya daga Nijeriya zuwa Kamaru.

‘Yanfashin sun sace mutanen ne a gaɓar tekun da ake kamun kifi mai suna Kombo Fishing Port da ke ɓanagren Kamaru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here
Prove your humanity: 10   +   4   =