Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarkin ƙasar a ranar Talata,
Gwamnan Kano zai koma jam’iyyar APC ranar Litinin
Tinubu ya yi alhinin rasuwar ɗan kasuwar Kano Bature Abdulaziz
Wannan shi ne karo na biyu da babban layin wutar ke fuskantar irin wannan matsala a shekarar 2026 wanda ya haifar da katsewar wutar lantarki a fannoni da dama na ƙasar.
Layin wutar ya fara lalacewa ne a ranar Juma’a da ta gabata.
Masana da hukumomi sun danganta lalacewar da tangarɗar na’ura da rashin cikakken gyare-gyare da kulawa ga manyan layukan wuta.
Bincike ya nuna cewa dukkanin tashoshin samar da wutar lantarki 23 da ke haɗe da babban layin sun daina aiki gaba ɗaya.
A halin yanzu, babu cikakken bayani kan abin da ya janyo wannan lalacewa.









