A ƙarshen makon jiya ne aka kammala taron da ƙungiyar addinin Musulunci ta Ansaruddeen, tare da hukumar gudanarwar ECOWAS su ka shirya a Najeriya da nufin haɗa kan malaman addinin musulunci da zamanantar da tsarin karatun allo
Wannan yunƙuri na da nufin yaƙi da tsatsauran ra’ayin aƙida tare da matsalar tsaron da ke addabar yankin yammacin Afrika.









