Fitattun ƴan ƙwallon Najeriya da ba za su buga gasar Afcon ta 2025 ba.
A makon da ya gabata ne mai horar da ƴanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya Éric Sékou Chelle ya fitar da sunayen ƴan ƙwallo 28 waɗanda za su wakilci ƙasar a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2025.
Kocin zai je gasar, wadda za a buga a ƙasar Morocco ne da zimmar samun nasara gagaruma bayan an yi waje da Najeriya a wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya ta 2026.
Daga cikin ƴan ƙwallon da Chelle ya fitar, akwai guda biyar da ba su taɓa wakiltar Najeriya a babbar tawaga ba, lamarin da ya janyo cece-kuce, a gefe ɗaya kuma wasu suke yaba masa da fito da sabbin ƴanwasa.
Sabbin ƴan wasa biyar ɗin su ne ɗan wasan baya Ryan Alebiosu da ɗan wasan tsakiya Ebenezer Akinsanmiro da Usman Muhammed da Tochukwu Nnadi waɗanda su ma duk ƴanwasan tsakiya ne, sai ɗan wasan gaba, Salim Fago Lawal.
Najeriya za ta buga wasanta na farko ne a ranar 23 ga Disamba, inda za ta fafata da ƙasar Tanzaniya a filin wasa na Sportif de Fès a birnin Fès.
Sai dai wani abu da ya ɗauki hankalin magoya bayan tawagar shi ne rashin ganin wasu fitattun ƴan ƙwallon ƙasar, a daidai lokacin da aka gayyaci sabbi, lamarin da ya janyo ake tafka muhawara.
Wannan ya sa BBC ta rairayo wasu zaratan ƴanƙwallon Najeriya da ake ganin akwai rawar da za su iya takawa a gasar in da an gayyace su.









