Home Afrika Najeriya ta ƙaryata zargin leken asiri kan jirgin sojinta a Burkina Faso...

Najeriya ta ƙaryata zargin leken asiri kan jirgin sojinta a Burkina Faso ‎

99
0

‎Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta musanta rahotannin da ke yawo cewa jirginta kirar C-130 da ya yi saukar gaggawa a birnin Bobo-Dioulasso na ƙasar Burkina Faso, yana gudanar da aikin leken asiri a ɓoye.

‎Rundunar ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya marar tushe, tana mai jaddada cewa jirgin na kan hanyarsa zuwa ƙasar Portugal ne domin a yi masa gyara. Ta ce saukar gaggawar da jirgin ya yi ya biyo bayan matsalar tsaro, kamar yadda dokokin sufurin jiragen sama na duniya suka tanada.

‎A cewar bayanan da jaridar The Nation ta rawaito, wata majiya a hedkwatar tsaron NAF ta tabbatar da cewa jirgin na ɗauke da dukkan takardun izini da suka dace, kuma an bi duka ƙa’idoji da matakan doka da suka shafi tafiye-tafiyen jiragen sama na soja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here
Prove your humanity: 1   +   6   =