Home Tsaro Amurka Za Ta Hana Biza Ga ‘Yan Najeriya Masu Hannu A Zargin...

Amurka Za Ta Hana Biza Ga ‘Yan Najeriya Masu Hannu A Zargin Kisan Kiristoci

104
0

Amurka ta yi barazanar saka takunkumai da hana bizar shiga ƙasarta ga duk wanda ta samu da hannu a zargin yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Ministan harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ne ya wallafa hakan a shafinsa na X
“Matakin, martani ne ga matsalar yi wa Kiristoci kisan gilla, zargin da bai bayar da wata hujja a kansa ba”. In ji Ministan.
A jiya Laraba ne wani kwamatin Majalisar Wakilan Amurka ya fitar da rahoto kan zargin, inda wasu ‘yanmajalisa suka nanata iƙirarin cewa ana kashe Kiristoci da gangan a Najeriya.
Najeriya dai ta sha musanta batun yiwa kiristoci kisan kiyashi, inda ta ce masu yada wannan Magana na son tada zaune ne kawai, tare da yi wa kasar nan makarkashiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here
Prove your humanity: 4   +   6   =